< Números 1 >

1 Y él Señor dijo a Moisés en el desierto del Sinaí, en la Tienda de la reunión, el primer día del segundo mes, en el segundo año después de que salieron de la tierra de Egipto.
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 Toma el número completo de los hijos de Israel, por sus familias y por las casas de sus padres, cada varón por nombre;
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 Todos los que tengan veinte años o más y puedan ir a la guerra en Israel deben ser contados por ti y Aarón por sus ejércitos.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 Y para ayudarte, toma a un hombre de cada tribu, el jefe de la casa de su padre.
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 Estos son los nombres de aquellos que serán tus ayudantes: de Rubén, Elisur, el hijo de Sedeur;
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 De Simeón, Selumiel, el hijo de Zurisadai;
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 De Judá, Najón, hijo de Aminadab;
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 De Isacar, Natanael, el hijo de Zuar;
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 De Zabulón, Eliab, hijo de Helón;
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 De los hijos de José: de Efraín, Elisama, hijo de Amiud; de Manasés, Gamaliel, el hijo de Pedasur,
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 De Benjamín, Abidán, hijo de Gedeoni;
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 De parte de Dan, Ahiezer, el hijo de Amisadai;
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 De Aser, Pagiel, el hijo de Ocrán;
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 De Gad, Eliasaf, hijo de Deuel;
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 De Neftalí, Ahira, el hijo de Enán.
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 Estos son los hombres nombrados de entre todas las personas, jefes de las casas de sus padres, jefes de las tribus de Israel.
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 Y tomaron Moisés y Aarón a estos hombres, escogidos por su nombre;
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 Y se reunieron todas las personas el primer día del segundo mes; y todos dejaron en claro a su familia y la casa de su padre, por el número de los nombres, de veinte años en adelante.
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 Como el Señor le había dado órdenes a Moisés, fueron contados por él en el desierto del Sinaí.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 Las generaciones de los hijos de Rubén, el hijo mayor de Israel, fueron contados por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años y más, que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 Cuarenta y seis mil quinientos de la tribu de Rubén fueron contados.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 Las generaciones de los hijos de Simeón fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 Cincuenta y nueve mil, trescientos de la tribu de Simeón estaban contados.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 Las generaciones de los hijos de Gad fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 Cuarenta y cinco mil seiscientos cincuenta de la tribu de Gad fueron contados.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 Las generaciones de los hijos de Judá fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 Setenta y cuatro mil seiscientos de la tribu de Judá fueron contados.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 Las generaciones de los hijos de Isacar fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 Cuarenta y cuatro mil cuatrocientos de la tribu de Isacar fueron contados.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 Las generaciones de los hijos de Zabulón fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 Cincuenta y siete mil cuatrocientos de la tribu de Zabulón estaban contados.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 Las generaciones de los hijos de José fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 Cuarenta mil quinientos de la tribu de Efraín fueron contados.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 Las generaciones de los hijos de Manasés fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 Treinta y dos mil, doscientos de la tribu de Manasés fueron contados.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 Las generaciones de los hijos de Benjamín fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 Treinta y cinco mil cuatrocientos de la tribu de Benjamín estaban contados.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 Las generaciones de los hijos de Dan fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 Se contaron sesenta y dos mil setecientos de la tribu de Dan.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 Las generaciones de los hijos de Aser fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 Cuarenta y un mil quinientos de la tribu de Aser fueron contados.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 Las generaciones de los hijos de Neftalí fueron contadas por sus familias y las casas de sus padres, todos los varones de veinte años o más que pudieron ir a la guerra;
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 Cincuenta y tres mil cuatrocientos de la tribu de Neftalí fueron contados.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 Estos son los que fueron contados por Moisés y Aarón y por los doce jefes de Israel, uno de cada tribu.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 Así que todos los que fueron contados de los hijos de Israel, por sus familias, todos los de veinte años o más que pudieron ir a la guerra,
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 Fueron seiscientos tres mil quinientos cincuenta.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 Pero los levitas, de la tribu de sus padres, no fueron contados entre ellos.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 Porque él Señor dijo a Moisés:
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 Sólo la tribu de Leví no será contada entre los hijos de Israel.
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 Los levitas, deben estar en el tabernáculo del testimonio, con sus recipientes y todo lo que contiene: deben transportar la Tienda, y ser responsables de todo lo que tenga que ver con ella, y colocar sus tiendas alrededor del tabernáculo.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 Y cuando la tienda de reunión avanza, los levitas deben derribarla; y cuando se debe colocar, deben hacerlo: cualquier persona extraña que se acerque a ella debe ser condenada a muerte.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 Los hijos de Israel pondrán sus tiendas, cada uno en su campamento alrededor de su bandera.
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 Pero las tiendas de los levitas deben estar alrededor de la tienda de la reunión, para que la ira no caiga sobre los hijos de Israel: la tienda de la reunión debe estar al cuidado de los levitas.
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 Entonces los hijos de Israel hicieron lo que el Señor le había ordenado a Moisés.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Números 1 >