< 2 Krönikeboken 2 >

1 Och Salomo satte sig före att bygga Herrans namne ett hus, och ett sins rikes hus;
Solomon ya ba da umarni don a gina haikali domin sunan Ubangiji da kuma fada wa kansa.
2 Och afräknade sjutiotusend män till bördor, och åttatiotusend timbermän uppå berget, och tretusend och sexhundrad befallningsmän öfver dem.
Ya ɗebi mutane dubu saba’in su zama’yan ɗauko, mutane dubu tamanin su zama masu fasa dutse a tuddai, da kuma mutane dubu uku da ɗari shida su zama masu lura da su.
3 Och Salomo sände till Hyram, Konungen i Tyro, och lät säga honom: Såsom du med minom fader David gjorde, och sände honom cedreträ, att han skulle bygga sig ett hus, der han uti bo skulle;
Solomon ya aika wannan saƙo ga Hiram sarkin Taya. “Ka aika mini gumaguman al’ul kamar yadda ka yi wa mahaifina Dawuda sa’ad da ka aika masa al’ul don yă gina fada yă zauna a ciki.
4 Si, jag vill bygga Herrans mins Guds Namne ett hus, att honom må helgadt varda, till att röka god rökverk för honom, och till alltid bereda skådobröd, och bränneoffer om morgon och afton, på Sabbather och nymånader, och på Herrans vår Guds högtider; till evig tid för Israel.
Yanzu ina shirin ginin haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, in kuma keɓe shi gare shi don ƙona turare mai ƙanshi a gabansa, don kuma ajiyar burodi mai tsarki kullum, da kuma don miƙa hadayun ƙonawa kowace safiya, kowace yamma, da a Asabbatai da Sababbin Wata, da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji Allahnmu. Wannan dawwammamiyar farilla ce don Isra’ila.
5 Och det hus, som jag bygga vill, skall vara stort; förty vår Gud är större än alle gudar.
“Haikalin da zan gina zai zama mai girma, domin Allahnmu ya fi dukan sauran alloli girma.
6 Men ho är dess mägtig, att han bygger honom hus? Ty himmelen och alla himlars himlar kunna icke begripa honom. Ho skulle då jag vara, att jag skulle bygga honom hus? Utan att man må röka för honom.
Amma wa zai iya gina haikali dominsa, shi wanda sammai, har ma da sama sammai, ba za su iya riƙe shi ba? To, wane ne ni da zan gina haikali dominsa, in ba dai wurin ƙona hadayu a gabansa ba?
7 Så sänd mig nu en vis man, till att arbeta på guld, silfver, koppar, jern, skarlakan, rosenrödt, gult silke, och den som kan utgrafva med de visa, som när mig äro i Juda och Jerusalem, hvilka min fader David beställt hafver.
“Saboda haka sai ka aiko mini da mutum wanda ya gwanince a aiki da azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, da kuma shunayya, da garura, da shuɗɗan zare, da wanda kuma ya gwanince da aikin sassaƙa, domin yă yi aiki tare da gwanayen mutane da nake da su a Yahuda da Urushalima, waɗanda mahaifina Dawuda ya tanada.
8 Och sänd mig cedreträ, furoträ och hebenträ af Libanon; förty jag vet, att dine tjenare kunna hugga trä på Libanon; och si, mine tjenare skola vara med dina tjenare;
“Ka kuma aika mini al’ul, fir da gumaguman algum daga Lebanon, gama na san cewa mutanenka sun gwanince a yakan katakai a can. Mutanena kuwa za su yi aiki tare da naka
9 Att man tillreder mig mycket trä; ty huset, som jag bygga vill, skall vara stort och härligit.
don su tanada mini katakai da yawa, domin haikalin da zan gina dole yă zama mai girma da kuma ƙasaitacce.
10 Och si, jag vill gifva dina tjenare timbermannomen, som trä hugga, tjugutusend corar stött hvete, och tjugutusend corar bjugg, och tjugutusend bath vin, och tjugutusend bath oljo.
Zan ba wa bayinka masu yankan katakai waɗanda suka yanka katako, garwa niƙaƙƙen alkama dubu ashirin, garwan sha’ir dubu ashirin da randunan ruwan inabi dubu ashirin da kuma randunan man zaitun dubu ashirin.”
11 Då sade Hyram, Konungen i Tyro, genom skrifvelse, och sände till Salomo: Derföre, att Herren hafver sitt folk kärt, hafver han gjort dig till Konung öfver dem.
Hiram sarkin Taya ya amsa ta wurin rubuta wasiƙa zuwa ga Solomon. “Domin Ubangiji yana ƙaunar mutanensa, ya naɗa ka sarkinsu.”
12 Och Hyram sade ytterligare: Lofvad vare Herren Israels Gud, som himmel och jord gjort hafver, att han gifvit hafver Konung David en visan, klokan och förståndigan son, som Herranom ett hus, och ett sins rikes hus bygga må.
Hiram ya ƙara da cewa, “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya yi sama da ƙasa! Ya ba Sarki Dawuda ɗa mai hikima, cike da wayo da kuma sani, wanda zai gina haikali domin Ubangiji da kuma fada wa kansa.
13 Så sänder jag nu en visan man, som förstånd hafver, nämliga Hyram Abiv;
“Zan aika maka Huram-Abi, wani gwani wanda ya iya aiki, kuma mai hikima,
14 Ene qvinnos son utaf Dans döttrar, och hans fader hade varit en Tyrer; han kan arbeta på guld, silfver, koppar, jern, sten, trä, skarlakan, gult silke, linnet, rosenrödt: och allahanda utgrafva, och göra allahanda konsteliga, det man honom föregifver, med dina visa, och med mins herras Konung Davids dins faders visa.
wanda mahaifiyarsa ta fito daga Dan, mahaifinsa kuma daga Taya. An horar da shi a aikin zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, dutse, itace, da kuma shuɗi, shunayya, garura, da lilin mai kyau. Ya gogu a kowane irin zāne-zāne, zai kuma iya yin kowane zānen da aka ba shi. Zai yi aiki tare da masu sana’arka, da kuma tare da waɗanda ranka yă daɗe, Dawuda mahaifinka ya tanada.
15 Så sände nu min herre hvete, bjugg, oljo och vin, till sina tjenare, såsom han sagt hafver;
“Yanzu fa, bari ranka yă daɗe, yă aiko wa bayinsa alkama da sha’ir da kuma man zaitun da ruwan inabin da ka alkawarta,
16 Så vilje vi hugga trä på Libanon, så mycket som behöfves, och vilje låta det lägga i flottar i hafvet, in åt Japho; dädan må du låta föra det upp till Jerusalem.
za mu kuwa yanka dukan gumagumai daga Lebanon da kake bukata za mu kuwa yi fitonsu ta teku, su gangara zuwa Yaffa. Za ka iya kwashe su daga can ka haura zuwa Urushalima.”
17 Och räknade Salomo alla främlingar i Israels land, efter det tal då David hans fader dem räknade; och vordo funne hundrade och femtio tusend, tretusend och sexhundrad.
Solomon ya ƙidaya dukan baƙin da suke cikin Isra’ila, bayan ƙidayan da mahaifinsa Dawuda ya yi; aka kuma tarar sun kai 153,600.
18 Och han gjorde af dem sjutiotusend dragare, och åttatiotusend huggare på bergena, och tretusend och sexhundrad befallningsmän, som folket vid arbetet höllo.
Ya sa 70,000 a cikinsu su zama’yan ɗauko, 80,000 kuma su zama masu fasan dutse a tuddai, sa’an nan 3,600 su zama shugabanni masu lura da aiki.

< 2 Krönikeboken 2 >