< Johannes 10 >

1 Sannerliga, sannerliga säger jag eder: Hvilken icke går in genom dörrena i fårahuset, utan stiger annorstäds in, han är en tjuf, och en röfvare.
“Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma.
2 Men hvilken som går in genom dörrena, han är herden till fåren.
Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne.
3 För honom låter dörravården upp, och fåren höra hans röst; och sin egen får kallar han vid namn, och leder dem ut.
Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje.
4 Och när han hafver släppt sin egen får ut, går han för dem, och fåren följa honom efter; ty de känna hans röst.
Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa.
5 Men den främmande följa de icke, utan fly ifrå honom; ty de känna icke deras röst, som främmande äro.
Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.”
6 Denna liknelsen sade Jesus till dem; men de förstodo icke hvad det var, som han sade dem.
Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.
7 Åter sade Jesus till dem: Sannerliga, sannerliga säger jag eder: Jag är dörren för fåren.
Saboda haka Yesu ya sāke cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ni ne ƙofar tumakin.
8 Alle de som för mig komne äro, de äro tjufvar och röfvare; men fåren hörde dem intet.
Duk waɗanda suka riga ni zuwa ɓarayi ne,’yan fashi kuma, amma tumakin ba su saurare su ba.
9 Jag är dörren; hvilken som ingår igenom mig, han skall blifva salig; och skall ingå och utgå, och finna bet.
Ni ne ƙofar; duk wanda ya shiga ta wurina zai sami ceto. Zai riƙa shiga yă fita yă kuwa sami wurin kiwo.
10 Tjufven kommer icke, utan till att stjäla, slagta och förgöra; jag är kommen, på det de skola hafva lif, och öfvernog hafva.
Ɓarawo yakan zo don yă yi sata ne kawai da kisa da kuma ɓarna. Ni kuwa na zo ne don su sami rai, su kuma same shi a yalwace.
11 Jag är den gode herden; den gode herden låter sitt lif för fåren.
“Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yakan ba da ransa domin tumakin.
12 Men den som lejder är, och icke är herden, hvilkom fåren icke tillhöra, ser ulfven komma, och öfvergifver fåren, och flyr; och ulfven bortrycker och förskingrar fåren.
Wanda aka ɗauko haya ba shi ne makiyayi mai tumakin ba. Saboda haka sa’ad da ya ga kyarkeci yana zuwa, sai yă sheƙa da gudu yă bar tumakin. Sai kyarkecin yă kai wa garken hari, yă kuma watsar da su.
13 Men den lejde flyr; ty han är lejd, och värdar intet om fåren.
Mutumin yakan gudu don shi ɗan haya ne kawai, bai kuwa damu da tumakin ba.
14 Jag är den gode herden, och känner min får, och min känna mig;
“Ni ne makiyayi mai kyau; na san tumakina, tumakina kuma sun san ni,
15 Såsom Fadren känner mig; och jag känner Fadren; och jag låter mitt lif för fåren.
kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uba, ina kuwa ba da raina domin tumakin.
16 Jag hafver ock annor får, som icke äro af detta fårahuset; dem måste jag ock draga härtill, och de skola höra min röst; och det skall varda ett fårahus och en herde.
Ina da waɗansu tumaki da ba na wannan garken ba ne. Dole ne in kawo su su ma. Za su saurari muryata, za su kasance garke guda ɗaya, makiyayi guda kuma.
17 Fördenskull älskar Fadren mig, att jag låter mitt lif, på det jag skall åter tagat igen.
Abin da ya sa Ubana yake ƙaunata ke nan, domin ina ba da raina, in ɗauko shi kuma.
18 Ingen tager det af mig; men jag låter det af mig sjelf; jag hafver magt att låta det, och jag hafver magt taga det igen. Detta budet fick jag af minom Fader.
Ba mai karɓe mini rai, ina dai ba da shi. Ina da iko in ba da shi, ina da iko in ɗauko shi kuma. Wannan umarni kuwa daga wurin Ubana na karɓo shi.”
19 Då vardt åter en tvedrägt ibland Judarna, för detta talets skull.
Saboda waɗannan kalmomi fa, sai ɓaraka ta sāke shiga cikin Yahudawa.
20 Månge af dem sade: Han hafver djefvulen, och är ursinnig; hvi hören I honom?
Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”
21 Somlige sade: Sådana ord äro icke dens mans, som djefvulen hafver; icke kan djefvulen öppna de blindas ögon.
Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
22 Så vardt då i Jerusalem kyrkomessa; och det var vinter.
Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
23 Och Jesus gick i templena, i Salomos förhus.
Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
24 Då kringhvärfde Judarna honom, och sade till honom: Huru länge förhalar du med oss? Säg oss fri, om du äst Christus.
sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
25 Jesus svarade dem: Jag hafver sagt eder det, och I tron det icke; gerningarna, som jag gör i mins Faders Namn, de bära vittne om mig.
Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
26 Men I tron det icke; ty I ären icke af min får, såsom jag sade eder.
Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
27 Min får höra mina röst, och jag känner dem, och de följa mig;
Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
28 Och jag gifver dem evinnerligit lif, och de skola icke förgås evinnerliga; ingen skall heller rycka dem utu mine hand. (aiōn g165, aiōnios g166)
Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn g165, aiōnios g166)
29 Min Fader, som mig dem gifvit hafver, är store än alle; och ingen kan rycka dem utaf mins Faders hand.
Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana.
30 Jag och Fadren ärom ett.
Da ni da Uba ɗaya ne.”
31 Då togo åter Judarna stenar, till att stena honom.
Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi,
32 Jesus svarade dem: Jag hafver många goda gerningar bevist eder af minom Fader; för hvilka af dem stenen I mig?
amma Yesu ya ce musu, “Na nuna muku ayyukan alheri masu yawa da Uba ya aiko ni in yi, a kan wanne kuke so ku jajjefe ni?”
33 Judarna svarade honom, och sade: För god gernings skull stene vi dig icke, utan för hädelsens skull; och att du, som äst en menniska, gör dig sjelf till Gud.
Yahudawa suka amsa suka ce, “Ai, ba don wani daga cikin waɗannan ayyukan alheri ne muke so mu jajjefe ka ba, amma don saɓon da kake yi, kai da kake mutum kawai, kana mai da kanka Allah.”
34 Jesus svarade dem: Är icke skrifvet i edor lag: Jag sade, I ären gudar?
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a cikin Dokarku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’?
35 Hafver han nu kallat dem gudar, till hvilka Guds ord skedde; och Skriften kan icke varda omintet;
Mun dai san Nassi ba ya ƙarya, In har ya kira su waɗanda maganar Allah ta zo musu, ‘alloli,’
36 Och I sägen dock till honom, som Fadren helgat hafver, och sändt i verldena: Du häder Gud; derföre, att jag säger: Jag är Guds Son?
to, game da wanda Uba ya keɓe a matsayin nasa ne ya kuma aiko shi duniya. Don me kuke ce saɓo nake, domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’
37 Gör jag icke mins Faders gerningar, så tror mig intet.
In ba ayyukan da Ubana yake yi ne nake yi ba, to, kada ku gaskata ni.
38 Men gör jag dem, tror då gerningomen, om I icke viljen tro mig; på det I skolen förstå, och tro, att Fadren är i mig, och jag i honom.
Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.”
39 Åter foro de efter att gripa honom; och han gick utu deras händer.
Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.
40 Och drog åter bort på hinsidon Jordan, till det rummet der Johannes hade först döpt; och blef der.
Sa’an nan Yesu ya sāke koma ƙetaren Urdun inda dā Yohanna yake baftisma. A can ya zauna
41 Och månge kommo till honom, och sade: Johannes gjorde intet tecken; men allt det Johannes om denna sagt hafver, är sant.
mutane da yawa suka zo wurinsa. Suka ce, “Ko da yake Yohanna bai yi wani abin banmamaki ba, duk abubuwan da Yohanna ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.”
42 Och trodde månge der på honom,
A nan kuwa mutane da yawa suka gaskata da Yesu.

< Johannes 10 >