< Johannes 6 >

1 Derefter for Jesus öfver det Galileiska hafvet, som är vid den staden Tiberias.
Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
2 Och mycket folk följde honom, derföre att de sågo hans tecken, som han gjorde med dem som sjuke voro.
sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
3 Och gick Jesus på ett berg, och satte sig der med sina Lärjungar.
Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
4 Och då tillstundade Påska, Judarnas högtid.
Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
5 Då lyfte Jesus upp sin ögon, och såg att mycket folk kom till honom, och sade till Philippum: Hvar få vi köpa bröd, att desse må äta?
Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
6 Det sade han till att försöka honom; ty han visste väl hvad han ville göra.
Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
7 Svarade honom Philippus: För tuhundrade penningar bröd vore dem icke nog, till att hvar finge ett litet stycke.
Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
8 Då sade till honom en af hans Lärjungar, Andreas, Simon Petri broder:
Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
9 Här är en pilt, som hafver fem bjuggbröd, och två fiskar; men hvad förslår det ibland så många?
“Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
10 Sade Jesus: Låter folket satta sig. Och på det rummet var mycket gräs. Då satte sig ned vid femtusend män.
Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 Och Jesus tog bröden, tackade, och fick Lärjungomen, och Lärjungarna skifte ibland dem som såto; sammaledes ock af fiskarna, så mycket han ville.
Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
12 Då de voro mätte, sade han till sina Lärjungar: Hemter tillhopa stycker, som öfverblifne äro, att de icke förfaras.
Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
13 Så hemte de tillhopa, och uppfyllde tolf korgar med styckom, som öfver voro af fem bjuggbröd, efter dem som ätit hade.
Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
14 När nu de menniskorna sågo, att Jesus hade gjort tecknet, sade de: Visserliga är denne den Propheten, som komma skall i verldena.
Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
15 När då Jesus förnam, att de ville komma och taga honom, och göra honom till Konung, gick han åter afsides bort uppå berget, han sjelf allena.
Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
16 Och när aftonen kom, gingo hans Lärjungar ned till hafvet;
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
17 Och stego till skepps, och foro öfver hafvet till Capernaum; och det var redo mörkt vordet, och Jesus var icke till dem kommen.
inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
18 Då blåste ett stort vader, och vågen begynte gå.
Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
19 När de nu rott hade vid fem och tjugu eller tretio stadier, fingo de se Jesum gå på hafvet, och nalkas skeppet; och de vordo förfärade.
Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
20 Då sade han till dem: Det är jag, rädens icke.
Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
21 Och de ville hafva tagit honom in i skeppet; och i det samma var skeppet vid landet, som de foro till.
Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
22 Dagen derefter, när folket, som stod på hinsidon hafvet, såg att der var intet annat skepp än det ena, som hans Lärjungar voro uti stegne; och att Jesus var icke instigen med sina Lärjungar i skeppet, utan hans Lärjungar voro bortfarne allena;
Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
23 Men annor skepp kommo af Tiberias, hardt till det rummet, der de hade ätit brödet, genom Herrans tacksägelse;
Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
24 När då folket såg, att Jesus var icke der, ej heller hans Lärjungar, stego de ock i skeppen, och kommo till Capernaum, och sökte Jesum.
Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 Och då de funno honom på hinsidon hafvet, sade de till honom: Rabbi, när komst du hit?
Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
26 Svarade Jesus dem, och sade: Sannerliga, sannerliga säger jag eder: I söken mig icke fördenskull, att I hafven sett tecken; utan fördenskull, att I hafven ätit af brödet, och ären vordne mätte.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
27 Verker icke den mat, som förgås, utan den som blifver till evinnerligit lif, den menniskones Son eder gifva skall; ty honom hafver Gud Fader beseglat. (aiōnios g166)
Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios g166)
28 Då sade de till honom: Hvad skole vi göra, att vi verka kunne Guds verk?
Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
29 Svarade Jesus, och sade till dem: Det är Guds verk, att I tron på den han sändt hafver.
Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
30 Då sade de till honom: Hvad tecken gör du då, att vi se kunne, och tro dig? Hvad verkar du?
Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
31 Våre fader åto Manna i öknene, som skrifvet är: Han gaf dem bröd af himmelen till att äta.
Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
32 Då sade Jesus till dem: Sannerliga, sannerliga säger jag eder: Icke gaf Mose eder det brödet af himmelen; men min Fader gifver eder det rätta brödet af himmelen.
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
33 Ty det är Guds bröd, som nederkommer af himmelen, och gifver verldene lif.
Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
34 Då sade de till honom: Herre, gif oss alltid detta brödet.
Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
35 Sade Jesus till dem: Jag är lifsens bröd; hvilken som kommer till mig, han skall icke hungra; och hvilken som tror på mig, han skall aldrig törsta.
Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
36 Men jag hafver sagt eder, att I hafven ock sett mig; och tron dock icke.
Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
37 Allt det min Fader gifver mig, det kommer till mig; och den till mig kommer, honom kastar jag icke ut.
Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
38 Ty jag är nederkommen af himmelen, icke att jag skall göra min vilja, utan hans vilja, som mig sändt hafver.
Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
39 Och det är mins Faders vilje, som mig sändt hafver, att jag intet borttappa skall af allt det han mig gifvit hafver; utan att jag skall uppväcka det på yttersta dagen.
Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
40 Detta är nu hans vilje, som mig sändt hafver, att hvar och en, som ser Sonen, och tror på honom, han skall hafva evinnerligit lif; och jag skall uppväcka honom på yttersta dagen. (aiōnios g166)
Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios g166)
41 Då knorrade Judarna deröfver, att han sade: Jag är det brödet, som nederkommet är af himmelen;
Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
42 Och sade: Är icke denne Jesus, Josephs son, hvilkens fader och moder vi känne? Huru säger han då: Jag är nederkommen af himmelen?
Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
43 Då svarade Jesus, och sade till dem: Knorrer icke emellan eder.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
44 Ingen kan komma till mig, utan Fadren, som mig sändt hafver, drager honom; och jag skall uppväcka honom på yttersta dagen.
Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
45 Det är skrifvet i Propheterna: De skola alle varda lärde af Gudi: Hvar och en, som det nu hört hafver af Fadren, och lärt det, han kommer till mig.
A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
46 Icke så, att någor hafver sett Fadren; utan den, som är af Gudi, han hafver sett Fadren.
Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
47 Sannerliga, sannerliga säger jag eder: Hvilken som tror på mig, han hafver evinnerligit lif. (aiōnios g166)
Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios g166)
48 Jag är lifsens bröd.
Ni ne burodin rai.
49 Edre fäder åto Manna i öknene, och äro blefne döde.
Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
50 Detta är det brödet, som nederkommer af himmelen, på det den deraf äter, skall icke dö.
Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
51 Jag är det lefvandes brödet, som nederkommer af himmelen; hvilken som äter af detta brödet, han skall lefva evinnerliga; och det brödet, som jag gifva skall, är mitt kött, hvilket jag gifva skall för verldenes lif. (aiōn g165)
Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn g165)
52 Då kifvade Judarna emellan sig, sägande: Huru kan denne gifva oss sitt kött till att äta?
Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
53 Sade Jesus till dem: Sannerliga, sannerliga säger jag eder: Utan I äten menniskones Sons kött, och dricken hans blod, då hafven I icke lif i eder.
Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
54 Hvilken som äter mitt kött, och dricker min blod, han hafver evinnerligit lif; och jag skall uppväcka honom på yttersta dagen. (aiōnios g166)
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios g166)
55 Ty mitt kött är den rätte maten, och min blod är den rätte drycken.
Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 Hvilken som äter mitt kött, och dricker min blod, han blifver i mig, och jag i honom.
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
57 Såsom lefvandes Fadren hafver mig sändt, och jag lefver för Fadrens skull; så ock den, som äter mig, han skall ock lefva för mina skull.
Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
58 Detta är det brödet, som af himmelen nederkommet är; icke såsom edre fäder åto Manna, och äro blefne döde; den som äter detta brödet, han skall lefva evinnerliga. (aiōn g165)
Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn g165)
59 Detta sade han i Synagogon, då han lärde i Capernaum.
Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
60 Men månge af hans Lärjungar, när de detta hörde, sade: Detta är ett hårdt tal; ho kan det höra?
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
61 Så, efter Jesus visste vid sig sjelf, att hans Lärjungar knorrade deröfver, sade han till dem: Förtörnar detta eder?
Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
62 Huru skall då ske, när I varden seende menniskones Son uppstiga, dit han förra var?
Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
63 Anden är den som gör lifaktig; köttet är intet nyttigt; de ord, jag säger eder, äro ande, och äro lif.
Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
64 Men någre af eder äro, som icke tro; ty Jesus visste väl af begynnelsen, hvilke de voro som icke trodde, och hvilken honom förråda skulle.
Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 Och han sade: Fördenskull sade jag eder, att ingen kan komma till mig, utan det varder honom gifvet af minom Fader.
Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
66 Ifrå den tiden gingo månge af hans Lärjungar tillrygga, och vandrade intet länger med honom.
Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
67 Då sade Jesus till de tolf: Icke viljen I ock gå bort?
Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
68 Svarade honom Simon Petrus: Herre, till hvem skole vi gå? Du hafver eviga lifsens ord; (aiōnios g166)
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios g166)
69 Och vi tro, och hafve förnummit, att du äst Christus, lefvandes Guds Son.
Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
70 Svarade dem Jesus: Hafver jag icke eder tolf utvalt? Och en af eder är en djefvul.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
71 Men det sade han om Juda Simons Ischarioth; ty han var den som honom förråda skulle, och var en af de tolf.
(Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)

< Johannes 6 >