< Jérémie 8 >

1 En ce temps-là, dit le Seigneur, on retirera de leurs sépulcres les os des rois de Juda, les os de ses princes, les os des prêtres, les os des prophètes, et les os des habitants de Jérusalem.
“‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
2 Et on les étalera pour qu'ils sèchent aux rayons du soleil, de la lune, de toutes les étoiles, et de toute l'armée céleste que ces hommes avaient aimés, qu'ils avaient servis, après lesquels ils avaient couru, auxquels ils s'étaient attachés et qu'ils avaient adorés. Et ces hommes, on ne pleurera plus sur eux, ils ne seront pas ensevelis et ils seront en exemple sur la face de la terre;
Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
3 Parce qu'ils ont préféré la mort à la vie, et ceux qui seront restés de cette race, en quelque lieu que ce soit, je les expulserai.
Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
4 Car voici ce que dit le Seigneur: Celui qui tombe ne se relève-t-il pas, et celui qui s'est détourné du chemin n'y revient-il pas?
“Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
5 Pourquoi donc mon peuple a-t-il dévié sans pudeur? pourquoi s'est-il opiniâtré dans son mauvais choix, et a-t-il refusé de se convertir?
To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
6 Maintenant prêtez l'oreille et écoutez: Nul ne se repent de sa méchanceté; en est-il qui diront: Qu'ai-je fait? Ils courent jusqu'à tomber dans leur course, comme un cheval trempé de sueur qui ne peut plus hennir.
Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
7 La grue dans le ciel connaît sa saison; la tourterelle, l'hirondelle des champs et le passereau observent le moment où ils couvent; mais mon peuple n'a pas connu les jugements du Seigneur.
Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
8 Comment direz-vous: Nous sommes sages, et la loi du Seigneur est avec nous? La plume menteuse de vos scribes écrit des erreurs;
“‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
9 Vos sages ont été confondus, et ils ont tremblé, et ils ont été pris, parce qu'ils ont rejeté la loi du Seigneur; quelle sagesse y a-t-il donc en eux?
Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
10 A cause de cela, je donnerai leurs femmes à d'autres, et leurs champs à des héritiers étrangers,
Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
11 Qui en recueilleront les fruits, dit le Seigneur; il n'y aura pas de raisins dans leurs vignes, pas de figues sur leurs figuiers, et les feuilles en tomberont.
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
12 Qui en recueilleront les fruits, dit le Seigneur; il n'y aura pas de raisins dans leurs vignes, pas de figues sur leurs figuiers, et les feuilles en tomberont.
Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
13 Qui en recueilleront les fruits, dit le Seigneur; il n'y aura pas de raisins dans leurs vignes, pas de figues sur leurs figuiers, et les feuilles en tomberont.
“‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
14 Pourquoi demeurons-nous en repos? Rassemblons-nous, et retirons-nous dans nos places fortes, et là soyons comme des rebuts, puisque le Seigneur nous a rejetés, et qu'il nous a abreuvés d'eau mêlée de fiel en punition de nos péchés envers lui.
Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
15 Nous nous attendions à la paix, et il ne nous est venu rien de bon; à la guérison, et voilà que c'était la souffrance.
Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
16 De Dan nous entendons le bruit de leur cavalerie rapide; toute la terre a tremblé au bruit des hennissements de ses chevaux; elle viendra, elle dévorera la terre et ses richesses, la ville et ses habitants;
Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
17 Car voilà que je vous envoie des serpents mortels contre lesquels il n'est point de charmes, et ils vous mordront,
“Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
18 Sans qu'il y ait de remède, et vous aurez en outre les douleurs de vos cœurs défaillants.
Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
19 J'entends les cris que jette, en une terre lointaine, la fille de mon peuple: Est-ce que le Seigneur n'est pas à Sion? est-ce qu'en Sion il n'y a plus de roi? Non, parce qu'ils m'ont exaspéré avec leurs idoles et leurs dieux étrangers.
Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
20 L'été est passé, la moisson est finie, et nous ne sommes point sauvés.
“Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
21 En mon angoisse, j'ai pris des vêtements de deuil en voyant l'affliction de la fille de mon peuple; j'ai été accablé de douleurs telles que celles de l'enfantement.
Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
22 N'y a-t-il plus de baume en Galaad? n'y a-t-il plus de médecin? D'où vient que la fille de mon peuple n'est point encore guérie?
Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?

< Jérémie 8 >